Saudiyya Za Ta Yanke Shawara Kan Makomar Hajjin 2020
Ministan harakokin lamurran addini da kuma haɗin kan addinai na Saudiyya Sahibzada Noor-ul-Haq Qadri ya ce a ranar Litinin ne 15 ga watan Yuni gwamnatin ƙasar za ta yanke shawara ta ƙarshe game da makomar Hajjin 2020.
Da yake bayani a wani taron tuntuba a ranar Alhamis, ministan ya ce gwamnatin Saudiyya za ta ɗauki matakin da ya fi dacewa saboda maniyyata aikin Hajji, sannan gwamnatin ta daɗe tana nazari tare da duba hanyoyi da dama game da aikin Hajjin.
Ya ce ana ci gaba da maharawa game da yadda za a tafiyar da aikin Hajjin a ma’aikatarsa, yana mai cewa Hajjin ba za ta kasance kamar yadda aka saba ba domin za a rungumi matakai na kaucewa yaɗuwar cutar korona.
Comments
Post a Comment